Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotu Ta Samu Nnamdi Kanu Da Laifin Ta’addanci

Kotun Tarayya da ke Abuja ta samu jagoran ƙungiyar IPOB da aka haramta, Nnamdi Kanu, da laifin ta’addanci bisa ƙarar da gwamnatin tarayya ta...




Kotun Tarayya da ke Abuja ta samu jagoran ƙungiyar IPOB da aka haramta, Nnamdi Kanu, da laifin ta’addanci bisa ƙarar da gwamnatin tarayya ta shigar.  

Mai Shari'a James Omotosho, yayin yanke hukunci, ya yanke duka muhimman batutuwa uku da aka gabatar a shari’ar nan a gaban masu ƙara.  

Alƙalin ya ce kalaman barazana da Kanu ke yi a cikin shirye-shiryen sa na watsa labarai sun haifar da fargaba da tashin hankali a zukatan jama’ar yankin Kudu maso Gabas.  

Ya ƙara da cewa, bisa hujjojin da masu gabatar da ƙara suka bayar, an gamsu da cewa akwai abubuwan da suka haɗa da laifin ta’addanci cikin abubuwan da aka gabatar da suka nuna niyyar Kanu da ayyukansa.  

Justice Omotosho ya bayyana cewa Kanu bai yi amfani da damar kare kansa ba, yana mai cewa, “ya ƙi kuma da gangan ya ƙauracewa gabatar da wata hujja da za ta wanke shi.”  

Kotun na ci gaba da yanke hukunci kan sauran ƙananan ƙididdigar tuhume-tuhume guda bakwai da ke kan Kanu.  

Cikakken bayani na nan tafe…

No comments