Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

NAF Ta Yi Wa ’Yan Ta’adda Mummunan Luguden Wuta a Sambisa Kwanaki Bayan Kashe Janar

Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya (NAF) ta sake cin nasara a yaƙin da ake yi da ta’addanci, bayan da ta kai wani gagarumin samame ta sama wand...




Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya (NAF) ta sake cin nasara a yaƙin da ake yi da ta’addanci, bayan da ta kai wani gagarumin samame ta sama wanda ya ragargaza sansanin ‘yan ta’adda a ARRA, cikin dajin Sambisa, ranar 19 ga Nuwamba, 2025.

Wata sanarwa da mai magana da yawun NAF, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar ta tabbatar da cewa an gudanar da harin ne bisa umarnin Shugaban Rundunar Sojin Sama, bayan gudanar da bincike da sa ido na tsawon lokaci. 

An gano al’amuran da ake zargi da kasancewar ‘yan ta’adda da ke da alaƙa da kwanton-bauna da aka yi wa sojojin ƙasa a yankin Kashomri, wanda hakan ya sa ake ta bin diddigi har zuwa ARRA.

Bayan samun ingantaccen bayanan sirri, rundunar sama ta fara luguden wuta ta hanyar da ta yi a tsari, tana kai hare-hare sau da dama har sai da ta cimma burinta.

NAF ta ce, dukkan manyan muhimman wuraren da aka nufa an same su gaba ɗaya, wanda hakan ya lalata ƙarfin gudanar da ayyukan ta’addanci da kuma rushe hanyoyin sadarwa da jigilar kayan aiki na ‘yan bindiga.

Mai magana da yawun rundunar ya ce, wannan harin ya nuna yadda NAF ke ci gaba da jajircewa wajen kare ƙasar, tallafa wa rundunar ƙasa da kuma matsa wa mayaƙan ta’addanci a dukkan fagen fama.

Samamen ya zo ne kwanaki kaɗan bayan kisan Birgediya-Janar Musa Uba, kwamandan runduna wanda ISWAP ta kashe bayan sun gano matsuguninsa ta hanyar kutse a bayanan sadarwa.

Lamarin ya faru ne lokacin da kwamandan da rundunarsa suka afka hanyar da aka dasa bama-bamai, lamarin da ya sa harin ya rikide zuwa musayar wuta mai zafi. Bayan ganin yadda lamarin ke ƙara dagulewa, Uba ya ja da baya cikin dabara sannan ya nemi tallafin sama.

Jiragen NAF suka bar wasu ayyuka suka nufi yankin don ceto rundunar, inda suka tarwatsa ‘yan ta’adda, suka kai dauki ga sojojin ƙasa da ma fararen hula na CJTF. Bayanai sun tabbatar da cewa an kashe yawancin ‘yan ta’adda yayin da rundunar sojin Nijeriya ta fuskanci ƙarancin asara.

Sai dai kisan Birgediya Uba ya sake bayyana irin haɗarin da ke kunno kai a fagen daga a Arewa maso Gabas, tare da nuna bukatar inganta tsarin tsaron bayanai da hanyoyin sadarwar rundunar, domin kauce wa cafke babban jami’i ko askari a irin waɗannan yanayin.

No comments