Shugaba Tinubu ya isa Nairobi, babban birnin ƙasar Kenya, a safiyar ranar Litinin, 11 ga Mayu, 2026, domin halartar taron "" (wand...
Shugaban Kenya, William Ruto, da Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, su ne suke jagorantar taron, wanda ya mayar da hankali kan sauya tattalin arziki, bunƙasa masana’antu masu amfani da hanyoyin kare muhalli, ƙirƙire-ƙirƙiren fasahar dijital, da cigaba mai ɗorewa.
Bayan haka, ana sa ran Shugaba Tinubu zai wuce Kigali, babban birnin ƙasar Ruwanda, domin halartar taron "Africa CEO Forum" da za a yi a ranakun 14 da 15 ga Mayu, 2026.
(Hotuna daga: AFP)



No comments