Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya Alhaji Murtala Sule Garo murnar rantsar da shi a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, wanda Gwam...
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya Alhaji Murtala Sule Garo murnar rantsar da shi a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, wanda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar a ranar Talata.
Gwamna Abba ya naÉ—a Murtala Garo ne domin cike gurbin da Comrade Aminu Abdulsalam ya bari, bayan murabus É—in da ya yi biyo bayan sauya sheÆ™ar gwamnan zuwa jam’iyyar APC.
Murtala Garo, mai shekara 48, gogajen É—an siyasa ne wanda ya riÆ™e muÆ™amai daban-daban, ciki har da Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo,Kwamishinan Ma’aikatar Ƙananan Hukumomi da Al’amuran Masarautu a Æ™arÆ™ashin gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, kuma É—an takarar Mataimakin Gwamna na jam’iyyar APC a zaben shekarar 2023.
Shugaba Tinubu ya jinjina wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa wannan naÉ—i, yana mai bayyana cewa matakin zai Æ™arfafa haÉ—in kan da ake buÆ™ata a cikin sahu da jerin mambobin jam’iyyar APC a Jihar Kano.
Haka zalika, Shugaban ya yi kira ga ɗaukacin masu ruwa da tsaki da su mara wa Gwamnan da mataimakin sa baya domin ciyar da jihar gaba. Ya kuma buƙaci sabon Mataimakin Gwamnan da ya yi aiki kafaɗa-da-kafaɗa da gwamna domin samar da shugabanci na gari da zai bunƙasa jihar.
A karshe, Shugaba Tinubu ya yi wa Murtala Garo fatan alheri a wannan sabon nauyi da aka dora masa.

No comments