Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Dala Biliyan 3 Don Yin Jirgin Ƙasa A Kano, Kaduna Da Legas

​Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta amince da bayar da kwangilar gina manyan ayyukan layin dogo guda uku a...

​Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta amince da bayar da kwangilar gina manyan ayyukan layin dogo guda uku a biranen Kano da Kaduna da kuma Legas, domin bunƙasa tattalin arziki da sauƙaƙa zirga-zirga.

​Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Taiwo Oyedele ne ya sanar da hakan ga manema labarai a fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC) da aka gudanar ranar Alhamis.

​Ministan ya bayyana cewa an zabo waɗannan biranen ne saboda matsayin su na cibiyoyin kasuwanci da suka dogara da kansu, inda ya ce zuba jari a cikinsu zai haifar da sakamako mai kyau ga rayuwar talakawa.

​Ayyukan da aka amince da su sun hada da:

​Birnin Kano: Za a gina layin jirgin ƙasa na cikin gari (Kano Metro City Rail) wanda zai riƙa ɗaukar mutane zuwa sassan birnin.

​Birnin Kaduna: Za a samar da tsarin jirgin ƙasa na "Light Rail" (wanda Gwamna Uba Sani ya nuna godiyar sa a kai a safiyar yau).

​Birnin Legas: Za a fara aikin layin jirgin ƙasa na "Green Line" (Phase 1A).

​Oyedele ya bayyana cewa waɗannan ayyuka guda uku za su ci kimanin dala biliyan 2.99 (kusan Naira tiriliyan hudu da rabi).

​Ya ƙara da cewa za a samar da kuɗaɗen ne ta hanyar kamfanin hannun jari na Ma'aikatar Kudin Ƙasa (MOFI), tare da haɗin gwiwar wasu hukumomin bayar da tallafi na musamman.

​"Mun sani cewa babu ci gaba ba tare da ingantattun hanyoyi da sufuri ba. Waɗannan ayyukan an tsara su ne don bunƙasa kasuwanci, sauƙaƙa wa ma’aikata da ɗalibai zirga-zirga, da kuma kyautata rayuwar jama’a a waɗannan manyan biranen," in ji Ministan.

​Wannan mataki na zuwa ne a matsayin wani bangare na shirin Shugaba Tinubu na tabbatar da cewa an farfaɗo da bangaren sufuri domin rage tsadar rayuwa da kuma samar da ayyukan yi ga matasa a fadin ƙasar nan.

​Masana tattalin arziki na ganin cewa idan aka kammala waɗannan ayyukan, birnin Kano da Kaduna za su zama manyan cibiyoyin sufuri a Arewacin Nijeriya, wanda hakan zai rage cinkoson ababen hawa da kuma saukaka jigilar kayan amfanin gona.
 

No comments