Daga Zubairu Lawal, LafiA Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Nasarawa ta bayyana goyon bayan ta ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu ...
Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Nasarawa ta bayyana goyon bayan ta ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin ya sake tsayawa takara karo na biyu a 2027, tare da jaddada Ĉudurin ta na gudanar da zabukan fidda ‘yan takara cikin gaskiya da adalci gabanin babban zabe.
Da yake jawabi ga manema labarai, Shugaban jam’iyyar na jiha, Hon. Aliyu Bello, ya ce APC ta tanadi cikakken tsari da zai tabbatar da cewa zabukan fidda ‘yan takara masu zuwa za su kasance cikin ‘yanci, gaskiya, kuma bisa cikakken bin dokar zabe da Ĉa’idojin jam’iyya.
Ya bayyana cewa an tsara dukkan matakan da za su kai ga zabukan fidda ‘yan takarar yadda za a tabbatar da haÉa kowa da kowa, adalci, da kuma ba duk masu ruwa da tsaki damar shiga, domin kara karfafa amincewa da tsarin.
Hon. Bello ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa abin da ya kira jagoranci mai Ĉarfi da sauyi, duk da Ĉalubalen tattalin arzikin duniya da ke fuskanta.
A cewar sa, gyare-gyaren da Shugaban ya aiwatar a fannoni masu muhimmanci kamar tattalin arziki, ababen more rayuwa, da tsaron Ĉasa sun kafa tubali mai Ĉarfi na ci gaba mai Éorewa da bunĈasar Ĉasa.
“Dangane da waÉannan nasarori, APC a Jihar Nasarawa tana goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tsayawa takara a 2027 domin ci gaba da gina kan nasarorin da aka samu,” in ji shi.
Jam’iyyar ta kuma bayyana cikakken amincewar ta da Gwamna Abdullahi Sule, inda ta yabawa gwamnatinsa bisa gagarumin ci gaba da aka samu a bangarorin ababen more rayuwa, fadada tattalin arziki, da shugabanci.
Hon. Bello ya ce jagorancin gwamnan ya Ĉarfafa haÉin kan jam’iyya tare da Ĉara wa jama’a Ĉwarin gwiwa a faÉin jihar.
Game da takarar gwamna ta 2027, APC ta amince da bayyanar Sanata Ahmed Aliyu Wadada a matsayin wanda Gwamna Sule ya fi so ya tsaya takara.
Jam’iyyar ta bayyana wannan mataki a matsayin sakamakon tuntuba mai zurfi da kuma dabara da ke nufin tabbatar da Éorewar ci gaba da kwanciyar hankali a shugabanci.
Duk da goyon bayan da ta nuna ga matsayin gwamnan, shugabancin jam’iyyar ya jaddada Ĉudurinsa na bin tsarin dimokuraÉiyya a cikin gida, tare da tabbatar da cewa za a bai wa dukkan masu neman takara dama iri daya.
Hon. Bello ya jaddada cewa ba za a tauye wa kowane dan takara haĈĈinsa ba, yana mai cewa za a gudanar da zabukan cikin gaskiya da adalci.
Shugaban APC ya buĈaci ‘ya’yan jam’iyya da masu ruwa da tsaki su ci gaba da kasancewa cikin haÉin kai tare da nuna halin dattaku a dukkanin harkokin siyasa.
Ya jaddada muhimmancin tattaunawa, mutunta juna, da bin dokokin jam’iyya, yana mai cewa hadin kai ne mabuÉin samun nasara a zaben 2027.

No comments