Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

2027: Jam'iyyar APC A Nasarawa Ta Nuna Goyon Bayan Ta Ga Shugaba Tinubu

Daga Zubairu Lawal, LafiA Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Nasarawa ta bayyana goyon bayan ta ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu ...

Daga Zubairu Lawal, LafiA

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Nasarawa ta bayyana goyon bayan ta ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin ya sake tsayawa takara karo na biyu a 2027, tare da jaddada Ĉ™udurin ta na gudanar da zabukan fidda ‘yan takara cikin gaskiya da adalci gabanin babban zabe.

Da yake jawabi ga manema labarai, Shugaban jam’iyyar na jiha, Hon. Aliyu Bello, ya ce APC ta tanadi cikakken tsari da zai tabbatar da cewa zabukan fidda ‘yan takara masu zuwa za su kasance cikin ‘yanci, gaskiya, kuma bisa cikakken bin dokar zabe da Ĉ™a’idojin jam’iyya.

Ya bayyana cewa an tsara dukkan matakan da za su kai ga zabukan fidda ‘yan takarar yadda za a tabbatar da haɗa kowa da kowa, adalci, da kuma ba duk masu ruwa da tsaki damar shiga, domin kara karfafa amincewa da tsarin.

Hon. Bello ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa abin da ya kira jagoranci mai Ĉ™arfi da sauyi, duk da Ĉ™alubalen tattalin arzikin duniya da ke fuskanta.

A cewar sa, gyare-gyaren da Shugaban ya aiwatar a fannoni masu muhimmanci kamar tattalin arziki, ababen more rayuwa, da tsaron Ĉ™asa sun kafa tubali mai Ĉ™arfi na ci gaba mai ɗorewa da bunĈ™asar Ĉ™asa.

“Dangane da waɗannan nasarori, APC a Jihar Nasarawa tana goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tsayawa takara a 2027 domin ci gaba da gina kan nasarorin da aka samu,” in ji shi.

Jam’iyyar ta kuma bayyana cikakken amincewar ta da Gwamna Abdullahi Sule, inda ta yabawa gwamnatinsa bisa gagarumin ci gaba da aka samu a bangarorin ababen more rayuwa, fadada tattalin arziki, da shugabanci.

Hon. Bello ya ce jagorancin gwamnan ya Ĉ™arfafa haɗin kan jam’iyya tare da Ĉ™ara wa jama’a Ĉ™warin gwiwa a faɗin jihar.

Game da takarar gwamna ta 2027, APC ta amince da bayyanar Sanata Ahmed Aliyu Wadada a matsayin wanda Gwamna Sule ya fi so ya tsaya takara.

Jam’iyyar ta bayyana wannan mataki a matsayin sakamakon tuntuba mai zurfi da kuma dabara da ke nufin tabbatar da ɗorewar ci gaba da kwanciyar hankali a shugabanci.

Duk da goyon bayan da ta nuna ga matsayin gwamnan, shugabancin jam’iyyar ya jaddada Ĉ™udurinsa na bin tsarin dimokuraɗiyya a cikin gida, tare da tabbatar da cewa za a bai wa dukkan masu neman takara dama iri daya.

Hon. Bello ya jaddada cewa ba za a tauye wa kowane dan takara haĈ™Ĉ™insa ba, yana mai cewa za a gudanar da zabukan cikin gaskiya da adalci.

Shugaban APC ya buĈ™aci ‘ya’yan jam’iyya da masu ruwa da tsaki su ci gaba da kasancewa cikin haɗin kai tare da nuna halin dattaku a dukkanin harkokin siyasa.

Ya jaddada muhimmancin tattaunawa, mutunta juna, da bin dokokin jam’iyya, yana mai cewa hadin kai ne mabuɗin samun nasara a zaben 2027.
 

No comments