Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Tinubu Ya Umurci Masu Riƙe Da Muƙaman Siyasa Da Ke Son Tsayawa Takara Su Yi Murabus Kafin 31 Ga Maris

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya umurci duk masu riƙe da muƙaman siyasa a ƙarƙashin gwamnatin sa da ke da niyyar tsayawa takara a zaɓuɓɓ...

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya umurci duk masu riƙe da muƙaman siyasa a ƙarƙashin gwamnatin sa da ke da niyyar tsayawa takara a zaɓuɓɓukan gama-gari na 2027 da su yi murabus daga muƙaman su kafin ko a ranar 31 ga Maris, 2026.

Wannan umurni ya yi daidai da tanade-tanaden Sashe na 88(1) na Dokar Zaɓe ta 2026, tare da jadawalin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kan ta ta Ƙasa (INEC) ta fitar dangane da zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasa kafin zaɓuɓɓukan 2027.

A cikin wata takarda da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya rattaba wa hannu, wadda Babban Sakatare na Babban Ofishin Ayyuka, Dakta Ibrahim Abubakar Kana, ya fitar, an bayyana cewa sharaɗin yin murabus ya shafi dukkan nau’o'in masu riƙe da muƙaman siyasa na shugaban ƙasa da ke son shiga zaɓen fidda gwani ko neman takara a kowane muƙamin zaɓe.

Waɗannan sun haɗa da: Minista, Ƙaramin Ministoci, Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman, Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa, Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa, Mataimaki na Kusa ga Shugaban Ƙasa, Darakta-Janar, da Shugaban Hukuma (CEO) na hukuma, kamfani, da cibiyar gwamnati na tarayya, tare da duk sauran masu riƙe da muƙaman siyasa na shugaban ƙasa.

Saboda haka, ana buƙatar duk wanda wannan umurni ya shafa da ya gabatar da takardun murabus ɗin sa ta hannun Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya kafin ko a ranar 31 ga Maris, 2026, ba daga baya ba.

Shugaba Tinubu ya jaddada cewa wannan mataki yana da muhimmanci domin tabbatar da cikakken bin dokokin zaɓe, ƙarfafa gaskiya a harkokin siyasa, da kuma samar da dama bai-ɗaya ga duk masu neman takara kafin zaɓuɓɓukan.

Ya kuma buƙaci duk masu ruwa da tsaki da su lura da wannan umurni tare da tabbatar da cikakken bin sa, yana mai jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ƙarfafa cibiyoyin dimokiraɗiyya da kuma inganta sahihancin zaɓuɓɓuka a Nijeriya.
 

No comments