Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya miƙa sunan Ambasada Ismail Abba Yusuf ga Majalisar Dattawa domin amincewa da shi a matsayin sabon shuga...
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya miƙa sunan Ambasada Ismail Abba Yusuf ga Majalisar Dattawa domin amincewa da shi a matsayin sabon shugaba kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON).
Rahotanni sun nuna cewa naɗin ya yi daidai da tanadin sashe na 3(2) na Dokar NAHCON ta 2026, inda aka isar da wasiƙar naɗin ga Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, a ranar Talata. A cikin wasiƙar, Shugaba Tinubu ya roƙi Majalisar ta gaggauta tantancewa tare da amincewa da nadin domin sabon shugaban ya fara aiki ba tare da ɓata lokaci ba.
Wannan mataki ya biyo bayan murabus ɗin tsohon Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman, wanda ya sauka daga muƙaminsa a farkon makon nan bayan kusan watanni 14 yana jagorantar hukumar. Ba a bayyana cikakkun dalilan murabus ɗin nasa ba, sai dai fadar shugaban ƙasa ta hanzarta cike gurbin domin kauce wa tangarda a tafiyar da ayyukan hukumar.
Ambasada Ismail Abba Yusuf gogaggen jami’in diflomasiyya ne da ya shafe shekaru da dama yana aiki a fagen hulɗar ƙasa da ƙasa da kuma hidimar gwamnati.
Kwanan nan ya kammala aikinsa a matsayin Jakadan Nijeriya a ƙasar Turkiyya daga 2021 zuwa 2024, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.
Masu lura da al’amura na kallon naɗin nasa a matsayin wani yunƙuri na sake farfaɗo da hukumar gabanin shirye-shiryen aikin Hajji mai zuwa. NAHCON na da muhimmiyar rawa wajen tsara, kulawa da kuma daidaita harkokin aikin Hajjin Musulman Nijeriya, ciki har da hulɗa da hukumomin Saudiyya, hukumomin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki.
Idan Majalisar Dattawa ta amince da naɗin, Ambasada Yusuf zai jagoranci shirye-shiryen aikin Hajji na gaba, tare da mai da hankali kan inganta walwalar alhazai, tabbatar da bin ƙa’idoji, da kuma ƙarfafa gaskiya da rikon amana a cikin hukumar.
Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta tsara ranar tantance shi cikin kwanaki masu zuwa, a matsayin wani ɓangare na aikinta na duba da tabbatar da nadin da shugaban ƙasa ya yi.

No comments