Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Yadda Aka Yanka ’Ya’ya Na Biyar Gaban Idanu Na A Yelwata – Wata Uwa

Wata mata da ta tsira daga mummunan harin Yelwata da aka kai a jihar Benuwe, Msurshima Apeh, ta bayyana gaban Majalisar Dokokin Amurka yadda...




Wata mata da ta tsira daga mummunan harin Yelwata da aka kai a jihar Benuwe, Msurshima Apeh, ta bayyana gaban Majalisar Dokokin Amurka yadda ta kalli ’ya’yanta biyar ana kashe su a gabanta yayin harin.

An ruwaito cewa ta gabatar da wannan shaida ranar Alhamis gaban kwamitin harkokin Afirka na Majalisar Wakilai, inda ake nazari kan matakin tsohon shugaban Amurka Donald Trump na maida Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ake kallon suna da matsalar take haƙƙin addini (CPC).

Ta ce maharan sun mamaye sansanin ’yan gudun hijira inda iyalai da dama ke kwana duk dare.

“Mun kwanta barci misalin ƙarfe tara na dare. Sai ga su — ’yan bindiga Fulani — sun afka inda muke kwana. An rufe mu a cikin sansanin Yelwata. Sun fara yanka mutane da takubba tare da harbi,” inji ta cikin bidiyo daga jihar Benuwe.

Ta ce bayan maharan sun gama kashe mutane da dama, sai suka zuba fetur a sansanin suka kunna wuta.

“Da suka rage kashewa, suka zuba man fetur a ginin, suka kuma kunna wuta. Mafi yawan mutane sun ƙone da ransu,” inji ta.

Apeh ta bayyana cewa don ta tsira sai ta hango wata bishiya, ta hau kanta, yayin da ’ya’yanta biyar suke kuka a ƙasa.

“Na hangi wata bishiya, na miƙa hannu na riƙe wani reshe, na hau sama na ɓoye. ’Ya’yana guda biyar suna ƙasa suna kuka, a gabana 'yan ta'addan suka yanka su ɗaya bayan ɗaya,” ta ce cikin murya mai cike da kuka.

Ta ce, daga bisani ta tsere cikin daji kafin masu ceto su gano ta su fito da ita.

“Haka na yi ta gudu a cikin daji har wasu suka zo suka ceto ni. Daga baya aka yaɗa mu zuwa wani sabon sansani,” inji ta.

Harin Yelwata ya faru ne a Yuni 2025 a karamar hukumar Guma ta jihar Benue. Rahotanni sun nuna cewa mutanen da suka mutu sun kai 100 har zuwa 200, yayin da fiye da mutane 3,000 suka rasa muhallansu. Yawancin masu tsira an tura su sansanonin Nasarawa.

Kungiyoyin kare hakkin bil’adama sun ce adadin mutanen da suka mutu na iya kaiwa 200, duk kuwa da adadin da gwamnati ta bayar. Majiyoyi na tsaro sun danganta harin ga wasu makiyayan da ke dauke da makamai.

Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan, ya ziyarci waɗanda suka ji rauni a asibitoci, sannan ya bada umarnin daukar matakin tsaro cikin gaggawa. Hukumar agajin gaggawa ta gargadi cewa iyalai da dama sun rage da matsaloli kamar karancin abinci, magani da kayan shimfiɗa.

Rundunar ’yan sanda daga bisani ta ce ta kama mutum 26 da ake zargi da hannu a harin.

Lamarin ya sake ƙara haska matsalar rikicin manoma da makiyaya da ya dade yana ci a yankin Middle Belt, wanda ya haɗu da zarge-zargen hare-haren da ake wa al’ummomi bisa bambancin addini.

Shaidar da Apeh ta bayar ta zo ne bayan Donald Trump ya mayar da Nijeriya cikin jerin CPC, tare da zargin cewa ana addabar Kiristoci a ƙasar. Ya kuma ce za a duba yiwuwar amfani da karfin soja.

Gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da zargin, inda Shugaba Tinubu ya ce ƙasar nan tana girmama ’yancin addini kuma ba ta nuna wariya ga kowane bangare ba.

No comments