Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Za A Yi Zaɓen Ƙananan Hukumomin Katsina A Watan Fabrairu, 2025

Daga Imrana Abdullahi Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Jihar Katsina ta sanar da ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025 a matsayin lokacin da za a ...

Daga Imrana Abdullahi

Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Jihar Katsina ta sanar da ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025 a matsayin lokacin da za a gudanar da zaɓen shugabannin Ƙananan Hukumomi da Kansiloli a duk faɗin Jihar.

Shugaban Hukumar,  Lawal Faskari ne ya bayyana hakan a wajen wani taron manema labarai da ya kira a Katsina, wanda ya samu halartar wakilan jam'iyyu da jami'an tsaro a Jihar. 

Ya ce an yi wannan sanarwar ne domin tabbatar da abin da doka ta tanadar a harkar zaɓe.

A lokacin zaɓen, ana sa ran samun zaɓen shugabannin Ƙananan Hukumomi 34 da Kansiloli 361 a ɗaukacin Jihar.

 

No comments