HOTO: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, FNIPR, ya karɓi baƙuncin Daraktan Sashen Yaƙi da Barazanar Zamani...
HOTO: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, FNIPR, ya karɓi baƙuncin Daraktan Sashen Yaƙi da Barazanar Zamani (Hybrid Threats Directorate) na Ma'aikatar Harkokin Waje da Raya Ƙasashen Waje ta Birtaniya (FCDO), Mista Jonny Hall, CMG, OBE, tare da wasu jami'an Birtaniya da ke aiki a Nijeriya, a lokacin wata ziyarar girmamawa da suka kai masa a ranar Talata, 24 ga Yuni, 2026, a Abuja.
Zaman nasu ya mayar da hankali ne kan batutuwan da ke da muhimmanci ga ɓangarorin biyu, ciki har da sadarwa ta dabaru, tabbatar da ingancin bayanai, da kuma haɗin gwiwa wajen tunkarar sababbin barazanar zamani da ke tasowa a fagen yaɗa bayanai ta kafafen dijital.



No comments