Rundunar Tsaro ta Kasa (DHQ) ta bayyana cewa dakarun kasar nan sun samu nasarar ragargazar dimbin ’yan ta’adda, inda suka kama wasu da dama ...
Wadannan nasarori sun faru ne a yayin ayyukan kakkaba da sojoji suka gudanar tsakanin ranar 30 ga watan Afrilu zuwa 7 ga watan Mayun 2026.
Daraktan Yada Labarai na Rundunar Tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abuja. Ga yadda nasarorin suke kasance a kowacce shiyya:
• Arewa maso Gabas (Operation HADIN KAI): Rundunar ta dakile hare-haren ’yan ta’adda a Magumeri da ke jihar Borno. Haka kuma, wasu daga cikin maharan sun mika wuya, yayin da aka kama masu kai musu kayan abinci da makamai.
• Arewa maso Yamma (Operation FANSAN YAMMA): Sojoji sun yi artabu da ’yan fashi a jihohin Katsina da Zamfara, inda aka kashe da dama tare da kwace babura da makamai.
• Arewa ta Tsakiya (Operation SAVANNAH SHIELD): An ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da kama masu safarar harsasai har guda 250 a cikin birnin Abuja.
• Jihar Filato: Jami'an tsaro sun bankado wata masana’antar kera makamai ba bisa ka’ida ba a Jos ta Kudu, inda aka kama mutanen da ake zargi da kera bindigogi.
• Jihar Benuwai da Kogi: An samu nasarar ceto wasu yara dalibai da aka sace daga gidan marayu.
Janar Onoja ya kara da cewa, dakarun Operation DELTA SAFE a Kudancin kasar da kuma Operation UDO KA a Kudu maso Gabas duk sun samu nasarar kama masu garkuwa da mutane da kuma dillalan makamai na kungiyar IPOB/ESN.
"Rundunar sojin kasa a karkashin jagorancin Shugaban Hafsun Tsaro, Olufemi Oluyede, ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa ’yan Najeriya sun rayu cikin lumana da kwanciyar hankali." — Maj. Gen. Onoja
Wannan gagarumar nasara ta nuna cewa jami’an tsaro sun sake zage damtse wajen ganin sun kawo karshen matsalolin tsaro da suka addabi sassan kasar nan.

No comments