Daga Ibrahim Muhammad, Kano A yayin da jam'iyyar ADC ke ci gaba da samun karbuwa da samun shigowar muhimman mutane manyan jagororin siy...
A yayin da jam'iyyar ADC ke ci gaba da samun karbuwa da samun shigowar muhimman mutane manyan jagororin siyasa cikin ta daga jam'iyyu daban-daban, wani jigo a cikin jam'iyyar da ya daÉe yana bada gudumawa wajen bunĘasata a jihar Kano daga Ęaramar Hukumar Dala, Ambasada Abdulrahman Mai Nasara Salga ya bayyana jin daÉin sa da yadda jam'iyyar ke samun karbuwa.
Ambasada Abdulrahman Salga, wanda ya yi takarar neman Éan majalisar tarayya a Ęaramar Hukumar Dala a 2023, ya ce abin farin ciki ne garesu irin bunĘasar da ake samu a jam'iyyar da suka jima suna ĘoĘarin ganin ta karbu ta tallata manufofin ta a tsakanin jama'a.
Ya ce, shigowar Dakta Rabiu Musa jagoran Kwankwasiyya da Éumbin magoya bayan sa, tare da shigowar tsohon mataimakin Gwamnan Kano, Ęwamared Aminu Abdulsalam, da dan takarar Gwamnan Kano a jam'iyyar APC a zaben 2023, Dokta Nasir Yusuf Gawuna, jam'iyyar ADC a nan Kano babban ci gaba ne da nasara ga jam'iyyar da ake ganinta Ęarama ce a baya, yanzu ta zama jam'iyyar adawa mafi Ęarfi a Ęasar nan.
Abdulrahman Mainasara ya ce su a matsayin su na yan jam'iyyar za su ci gaba da abin da suke yi na ganin al'umma sun karbe ta, suna fata jiga-jigan shugabanni da suke a jam'iyyar tun daga kan tsohon mataimakin shugaban Ęasa, Atiku Abubakar da Peter Obi da Kwankwaso da sauran jagorori za su haÉa kai, a sanya mafitar Ęasar nan a gaba domin kai wa ga nasara a zaben 2027 mai zuwa.

No comments