Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Shugaba Tinubu Ya Amince Da Tura Jakadu 65 Zuwa Ƙasashen Duniya

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da tura sabbin Jakadu 65 na Nijeriya zuwa ƙasashe daban-daban na duniya da kuma Majalisar Dinkin...

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da tura sabbin Jakadu 65 na Nijeriya zuwa ƙasashe daban-daban na duniya da kuma Majalisar Dinkin Duniya.

Sanarwar da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Juma’a ta bayyana cewa Jakadun sun haɗa da ma’aikatan diflomasiyya 31 (career ambassadors) da kuma waɗanda ba ma’aikatan diflomasiyya ba 34 (non-career ambassadors).

Majalisar Dattawa ta riga ta tabbatar da sunayen jakadun a watan Disambar bara.

Daga cikin waɗanda aka tura akwai:

Senata Grace Bent – Jakadiya a Lome, Togo

Sanata Ita Enang – Jakada a Afirka ta Kudu

Victor Ikpeazu – Spain

Nkechi Linda Ufochukwu – Tel Aviv, Isra’ila

Mahmud Yakubu – Qatar

Reno Omokri – Mexico

Aminu Dalhatu – Babban Kwamishina a Birtaniya

Janar Abdulrahman Bello Dambazau mai ritaya – China

Lateef Kayode Are – Amurka

Femi Fani-Kayode – Jamus

Yakubu N. Gambo – Saudiyya

Jimoh Ibrahim – Babban Wakilin Nijeriya a Majalisar Ɗinkin Duniya.

A bangaren jakadun ma’aikatan diflomasiyya kuwa, gwamnati ta tura su zuwa kasashe daban-daban ciki har da:

Mohammed Mahmud Lele – Algeria

Ahmed Mohammed Monguno – Masar

Muhammad Saidu Dahiru – India

Abdussalam Habu Zayyad – Senegal

Shehu Ilu Barde – Ghana

Aminu Nasir – Ethiopia

Haidara Mohammed Idris – Netherlands

Bako Adamu Umar – Morocco

Sulu Gambari Olatunji Ahmed – Malaysia

Ibrahim Danlami – Kenya

Adebayo Emmanuel Ayeni – Belgium

Wahab Adekola Akande – Switzerland

Bello Dogon-Daji Haliru – Thailand, da sauransu.

Sanarwar ta kara da cewa Birtaniya ta riga ta bayar da amincewar diflomasiyya (agrément) ga Babban Kwamishinan Najeriya mai jiran gado, Aminu Dalhatu.

Haka kuma Faransa ta amince da Ayo Oke a matsayin Jakadan Nijeriya a ƙasar.

Ma’aikatar Harkokin Waje ta sanar da sauran kasashen da aka tura jakadun zuwa, tare da neman amincewarsu kamar yadda tsarin diflomasiyya ya tanada.

Shugaba Tinubu ya kuma umarci ma’aikatar da ta gaggauta shirya shirin horaswa (induction programme) ga dukkan jakadun kafin su kama aiki a ofisoshin jakadancin Nijeriya a faɗin duniya.
 

No comments