Ministan Kudi da Tattalin Arzikin Kasa, Wale Edun, ya yi maraba da sabbin bayanai daga Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) da ke nuna cewa tatta...
Wannan shi ne karo na biyu a cikin shekaru goma, idan ban da habakar da aka samu bayan cutar COVID-19, da aka samu habakar tattalin arziki fiye da kashi 4%. Wannan habakar ta biyo bayan karuwar kashi 4.23% da aka samu a zango na biyu na shekarar 2025, wanda ya nuna cigaba daga kashi 3.76% da aka samu a zango na uku na shekarar 2024.
Wannan cigaban ya nuna karuwar kwanciyar hankali a tsarin tattalin arziki da kuma tasirin sauye-sauyen da ake yi karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
An samu habaka a manyan bangarorin tattalin arziki guda uku a karshen shekarar 2025 da suka haɗa da:
• Aikin Gona: Ya habaka da kashi 4.0%, idan aka kwatanta da kashi 2.54% a karshen shekarar 2024. An samu wannan habakar ne saboda ingantuwar tsaro a yankunan da ake samar da abinci da kuma samun saukin samun kayayyakin noma.
• Masana'antu: Sun habaka da kashi 3.88%, idan aka kwatanta da kashi 2.49% a daidai irin wannan lokacin a shekarar 2024. An samu wannan habakar ne saboda ingantuwar hada-hadar kudaden kasashen waje, sauye-sauye a fannin makamashi, da kuma karuwar kwarin gwiwar masu zuba jari.
• Ayyukan Masu Zaman Kansu: Sun habaka da kashi 4.15%, wanda ya nuna cigaban habaka a fannin kudi, sadarwa, ciniki, da kuma fasahar zamani.
Kimanin bangarori 30 ne suka samu habaka fiye da kashi 3%, wanda ya nuna fadin habakar tattalin arzikin kasa da kuma karuwar rarrabuwarsa.
A dukkan shekarar 2025, tattalin arzikin Najeriya ya habaka da kashi 3.87%, idan aka kwatanta da kashi 3.38% a shekarar 2024. Girman tattalin arzikin kasar ya karu zuwa Naira tiriliyan 441.5, idan aka kwatanta da Naira tiriliyan 372.8 a shekarar 2024.
Wannan habakar ta nuna ingantuwar hadin kai a bangaren kasafin kudi, kiyaye kudaden kashewa, karfafa hanyoyin samun kudaden shiga, da kuma cigaba da sauye-sauyen tsarin tattalin arziki don maido da sahihancin tattalin arziki.
Ministan ya kara da cewa wannan bayanan suna karfafa kwarin gwiwar masu zuba jari na gida da na waje, kuma suna nuna cewa shirin sauye-sauyen Najeriya yana samun nasara.
Ma'aikatar Kudi tana ci gaba da jajircewa wajen aiwatar da sauye-sauye, daidaiton hukumomi, da kuma tattaunawa ta gaskiya tare da masu ruwa da tsaki.

No comments