Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya nuna damuwa sosai kan janye dakarun soji daga harabar Makarantar Sakandaren ’Yan Mata ta Maga, inda ’ya...
Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya nuna damuwa sosai kan janye dakarun soji daga harabar Makarantar Sakandaren ’Yan Mata ta Maga, inda ’yan bindiga suka mamaye suka sace ɗalibai 36, mintuna kaɗan bayan barin jami’an tsaro wurin.
Ya bayyana wannan damuwa ne a Birnin Kebbi a ranar Juma’a yayin da yake tarbar shugaban NLC, Joe Ajaero, wanda ya ziyarci jihar domin jajantawa bisa harin da aka kai.
A cewar gwamnan, gwamnati ta samu bayanan sirri cewa ana shirin kai hari a yankin, kuma hakan ya sa suka kira taron gaggawa da hukumomin tsaro domin dalile barazanar.
Rahotannin kuma sun tabbatar masa cewa za a tura jami’an tsaro isassu don kare makarantar.
Idris ya ce an tura sojoji zuwa wurin kamar yadda aka yi alƙawari, amma daga baya suka bar matsayinsu bayan ƙarfe 3 na safe — mintuna 45 kafin ’yan bindiga su kai harin misalin 3:45 na safe.
Ya jaddada cewa: “An tura sojoji kamar yadda aka tsara, amma daga baya suka janye da ƙarfe 3 na safe, sannan da 3:45 na safe abin ya faru.”
Ya ce gwamnatin jihar na neman cikakken bayani kan wanda ya bayar da umarnin janye jami’an tsaron a daidai lokacin da rahotanni ke nuna yiwuwar barazana.
Gwamnan ya kuma tabbatar wa jama’a cewa gwamnatin jiha tare da gwamnatin tarayya na aiki tuƙuru don ganin an ceto daliban da aka sace cikin koshin lafiya. Ya ce Shugaba Bola Tinubu ya nuna cikakkiyar damuwa, inda ya tura Mataimakin Shugaba, Kashim Shettima, zuwa jihar, yayin da Ministan Tsaron Jiha, Bello Matawalle, ya koma Kebbi domin jagorantar kokarin ceto yaran.
Idris ya ce an kuma umarci malamai da limamai su ƙara yawaita addu’o’i domin samun zaman lafiya da kubutar da daliban. Ya nuna damuwa kan yadda hare-hare ke ƙaruwa a sassan ƙasar nan, yana mai cewa hakan na iya zama aikin “makiyan gwamnati”, don haka ya bukaci jama’a su kasance masu addu’a da kwarin gwiwa.
Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayyana sace daliban a matsayin abin takaici ƙwarai, musamman a lokacin da jihar ke samun cigaba karkashin mulkin Idris. Ya ce abin da ya faru ba kamar abin da ya zo da bazata bane, yana mai gargadi cewa duk wani shiri na dakile cigaban jihar “ba zai yi nasara ba.”
Ajaero ya kara da cewa ƙungiyarsu za ta sake duba manufofinta domin goyon bayan ƙoƙarin ƙasa wajen tsaurara tsaro a makarantun da iyakoki. Ya ce za su tsara sabon tsari da zai inganta matakan kare makarantu daga hare-hare a nan gaba.
Lamarin ya faru ne tsakanin ranar Lahadi 9 ga Nuwamba zuwa Alhamis 13 ga Nuwamba, abin da ya sa mazauna da dama tserewa daga gidajensu saboda tsoron ƙarin hare-hare.

No comments