Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

CANJA HAFSOSHIN TSARO: ADC Na Zargin Gwamnati Da Boye Gaskiya Kan Yunƙurin Juyin Mulki

Jami’iyyar ADC ta nemi Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana wa ’yan Nijeriya ainihin dalilan da suka sa aka tsige hafsoshin tsaro kwatsam, t...



Jami’iyyar ADC ta nemi Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana wa ’yan Nijeriya ainihin dalilan da suka sa aka tsige hafsoshin tsaro kwatsam, tana mai cewa wannan sauyi na gaggawa ya haifar da tambayoyi game da gaskiya da kwanciyar hankali a cikin gwamnatin kasa.

A ranar Juma’a ne Fadar Shugaban Ƙasa ta tabbatar da cewa an tsige Janar Christopher Musa, wanda shi ne Babban Hafsan Tsaro, tare da wasu manyan hafsoshi.

A cewar wata sanarwa daga Sunday Dare, Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, an maye gurbin Musa da Janar Olufemi Oluyede, wanda kafin wannan lokaci shi ne Babban Hafsan Sojojin Ƙasa.

Mejo-Janaru W. Shaibu shi ne sabon Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, yayin da Air Vice Marshal S.K. Aneke ya zama sabon Babban Hafsan Sojin Sama, sai kuma Rear Admiral I. Abbas da aka naɗa a matsayin Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa.

Sai dai Mejo-Janaru E.A.P Undiendeye, Babban Hafsan Leken Asiri na Soji, ya ci gaba da rike mukaminsa.

Wannan sauyi ya zo ne bayan rahotannin da ke cewa Hedikwatar Tsaro (DHQ) ta kama wasu jami’an soja ciki har da Brigediya Janar da Kanal, bisa zargin shirin juyin mulki a kan gwamnatin Tinubu.

“Ku faɗa wa ‘yan kasa gaskiyar dalilin tsige hafsoshin” – ADC

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran Jam’iyyar ADC, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, jam’iyyar ta bayyana damuwa da cewa sauyin ya biyo bayan rade-radin yunƙurin juyin mulki.

Ya ce, “Ko da yake mun san cewa Shugaban Ƙasa na da ikon yin irin wannan sauyi a matsayin Babban Kwamandan Rundunar Soji, abin damuwa ne ganin an yi hakan daidai lokacin da ake ta rade-radin yunƙurin juyin mulki.”

Jam’iyyar ta ce martanin gwamnati kan rade-radin bai da cikakkiyar fahimta, kuma ya nuna rikicewa a maimakon bayyana gaskiya.

Ta ƙara da cewa, “Yawancin hafsoshin da aka tsige sun shafe kusan watanni 28 kacal a mukamansu, yayin da Janar Musa kansa aka nada shi Babban Hafsan Soji shekara guda da ta gabata. Wannan irin sauyi yana da tasirin da ya shafi tsarin tsaro gaba ɗaya, don haka ba zai yiwu a yi shi ba tare da dalilai masu ƙarfi ba.”

ADC ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta bayyana gaskiya ga al’umma game da abin da ya faru, tana mai cewa matsayin jam’iyyar a matsayin adawa ba ya nufin son jefa ƙasar cikin rikici, illa dai ta na neman stability da kare dimokuraɗiyya.

Jam’iyyar ta kuma nuna damuwa da yadda tsaro ke tabarbarewa a wasu sassan ƙasar, inda ‘yan ta’adda ke dawowa, yayin da barayin daji ke ƙara karfi.

“Gwamnatin Tinubu ta fi mai da hankali kan siyasar mulki fiye da tsaron rayukan ‘yan ƙasa,” inji jam’iyyar.

Ta ƙara da cewa wannan sauyin gaba ɗaya a manyan hafsoshin soji, maimakon ya kawo kwanciyar hankali, zai ƙara zuga jita-jita da hasashe.

“Sauyin hafsoshin zai ƙarfafa tsarin tsaro” – Tinubu

A gefe guda, Shugaba Bola Tinubu ya wallafa a shafinsa na sada zumunta cewa an yi sauyin ne domin “ƙarfafa tsarin tsaro na ƙasa da ƙara inganta kariya ga ‘yan Nijeriya.”

No comments