Mayaƙan Boko Haram sun kashe wani hafsan soja da wasu ’yan sa-kai biyu a wani ƙazamin hari a sansanin sojoji a Jihar Borno. Wata majiyar soj...
Mayaƙan Boko Haram sun kashe wani hafsan soja da wasu ’yan sa-kai biyu a wani ƙazamin hari a sansanin sojoji a Jihar Borno.
Wata majiyar soji ta shaida mana cewa an kasa ɗauko gawar waɗanda aka kashe, saboda tsananin faɗan da aka gwabza da misalin ƙarfe 1 na dare a sansanin da ke yankin Krenowa a Ƙaramar Hukumar Marte ranar Asabar.
Ta ƙara da cewa, maharan sun lalata wata motar yaƙi, amma direbanta ya tsira da rauni a ƙafarsa, sannan sojoji fiye da 100 tare da makamai da sauran kayan aikinsu sun janye zuwa garin Marte.
Wasu majiyoyi sun shaida w manema labarai cewa mayaƙan Boko Haram sun kai wa sojojin hari ne kwanaki biyar bayan sojojin sun ƙwace sansanin ƙungiyar da ke Krenowa a ƙoƙarin sojojin na kakkaɓe ’yan ta’adda.
No comments