Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Dole Nnamdi Kanu Ya Fuskanci Shari'a - Kotun Koli

Kotun Ƙoli ta amince da buƙatar Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da ke ƙalubalantar hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara na soke tuhume-tuhumen da ake yi ...



Kotun Ƙoli ta amince da buƙatar Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da ke ƙalubalantar hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara na soke tuhume-tuhumen da ake yi wa Nnamdi Kanu, jagoran ƙungiyar IPOB.

Kotun Ƙolin ta ce, dole ne Kanu ya fuskanci shari'a.

A watan Oktoban bara ne, wata kotun ɗaukaka ƙara ta bayar da umarnin a saki Kanu inda ta ce akwai kura-kurai a shari'ar.

Sai dai gwamnati ta sake shigar da ƙara inda ta ce Kanu barazana ne ga tsaron Nijeriya.

No comments