Ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NDC, Peter Obi ya zargi Gwamnatin Tarayya da ƙulla maƙarƙashiyar hana shi yin takara a zaɓen shekarar...
Ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NDC, Peter Obi ya zargi Gwamnatin Tarayya da ƙulla maƙarƙashiyar hana shi yin takara a zaɓen shekarar 2027.
Yayin da yake jawabi a wani shirin horas da shugabanci da Ƙungiyar ‘NextGen Mentorship and Leadership Initiative‘ ta shirya a Jami’ar Madonna da ke Okija a Jihar Anambra ranar Juma’a, Obi ya yi iƙirarin cewa ana yin iƙirarin dakatar da shi daga shiga zaɓe mai zuwa.
“Idan na gaya muku abubuwan da nake fuskanta a yau, ba za ku ganni a nan ba. Mutane sun tambaye ni, ‘Shin har yanzu za ka je Madonna?’ Sai na ce, ‘Eh. Zan je.’ Suka ce da duk abubuwan da ke faruwa a Nijeriya, har yanzu za ka je can, sai na ce, ‘Eh. Na ga mafi muninsa.’ A yau, Gwamnatin Tarayyar Najeriya tana yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa ban zama ɗan takara a wannan zaɓen ba, amma ina gaya muku cewa ba za su yi nasara ba.”
“Idan kana rayuwa a inda babu ƙalubale, to ba ka rayuwa ne. Kada ku kalli ƙalubale, ƙalubale za su kasance a koyaushe. Ni ba ƙalubale nake kallo ba, burina shi ne inda na dosa. Na fi mayar da hankali ne kan sakamako mai kyau na inda na dosa, kuma hakan shi ne abin da yake ba ni ƙwarin gwiwa,” inji shi.
Haka kuma Obi ya ƙalubalanci dukkan masu neman takarar shugaban ƙasa, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, da su fito muhawarar bainar jama’a kan tsare-tsaren da suke da shi ga ƙasar.
“Ina ƙalubalantar duk wani mai takara da ya fito mu yi muhawara don ya faɗi abin da yake son yi wa wannan ƙasa, ciki har da Shugaba Bola Tinubu. Ba don na faranta muku rai nake faɗin hakan ba, a’a, don a canza Nijeriya kuma a gyara ta,” in ji shi.
Tsohon Gwamnan na Jihar Anambra ya shaida wa ɗaliban cewa ba burin kansa ba ne yake yi, a’a, don muradin ganin ƙasar ta gyaru ne.
Haka kuma Obi ya yi tsokaci game da hukuncin Babbar Kotun Tarayya wadda ta soke wani hukunci na baya da ke umartar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta yi rajistar Jam’iyyar NDC a matsayin jam’iyyar siyasa.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wata Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta soke hukuncinta na baya wanda ya umarci INEC da ta yi rajistar NDC a matsayin jam’iyyar siyasa.

No comments