Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Sauya Hafsoshin Tsaro Ba Ya Da Alaƙa da Jita-jitar Juyin Mulki – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa sauye-sauyen da Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi a manyan hafsoshin tsaro na ƙasar ba su da wata alaka da...



Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa sauye-sauyen da Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi a manyan hafsoshin tsaro na ƙasar ba su da wata alaka da jita-jitar juyin mulki da ta yadu kwanakin baya, inda ta ce matakin ya kasance tsari ne na dabarun tsaro domin ƙarfafa ayyukan tsaron ƙasa.

A makon da ya gabata, shugaban ƙasa ya amince da naɗin Janar Olufemi Oluyede a matsayin sabon Babban Hafsan Tsaro (CDS), wanda ya maye gurbin Janar Christopher Gwabin Musa. Haka kuma ya naɗa Manjo Janar W. Shaibu a matsayin Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Air Vice Marshal S.K. Aneke a matsayin Babban Hafsan Sojan Sama, da kuma Rear Admiral I. Abbas a matsayin Babban Hafsan Sojan Ruwa, yayin da Manjo Janar E.A.P. Undiendeye ya ci gaba da zama Babban Daraktan Leken Asirin Tsaro (CDI).

Wannan sanarwar na ƙunshe ne cikin wata takarda da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yada labarai, Sunday Dare, ya fitar, inda ya bayyana cewa sabbin naɗe-naɗen sun fara aiki nan take.

Sai dai sauye-sauyen sun zo ne kwana kaɗan bayan wani rahoto na kafar intanet da ya yi zargin cewa wasu jami’an soja sun shirya juyin mulki a kan gwamnatin Tinubu, lamarin da Hedikwatar Tsaro (DHQ) ta karyata da ƙarfi.

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan dabarun yada labarai, Bayo Onanuga, ya ce babu wata alaƙa tsakanin wannan sauyi da jita-jitar juyin mulki.

“Shugaban ƙasa yana da cikakken ikon naɗa ko sauke hafsoshin tsaro. Shi ne Kwamandan Sojojin Ƙasa baki ɗaya, kuma wannan ikon nasa ne na doka,” inji Onanuga.

Haka kuma, Tope Ajayi, wanda shi ma mai ba shugaban ƙasa shawara ne kan harkokin yada labarai, ya ƙara da cewa,

“Wannan ba martani ba ne ga jita-jita. Shugaban ƙasa ne kawai ke aiwatar da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi. Hafsoshin sun shafe kusan shekaru biyu suna aiki.”

Ajayi ya ce shugaba Tinubu yana son ya shigar da sabbin hangen nesa, kuzari da dabaru a cikin ayyukan yaƙi da ta’addanci, ‘yan bindiga, masu sace mutane da kuma ƙungiyoyin rarrabuwar kai.

A baya, Hedikwatar Tsaro ta bayyana rahoton juyin mulkin da ake yaɗawa a matsayin ƙarya ce wadda aka ƙirƙira don tayar da hankalin jama’a, tare da bayyana cewa jami’an da ake tsare da su na fuskantar bincike ne kan takatsantsan da rashin ladabi, ba saboda wani shirin kifar da gwamnati ba.

Ajayi ya kuma bayyana cewa matsalolin tsaro na dogon lokaci sun lashe kuɗaɗen kasafin ƙasa fiye da kima a cikin shekaru goma sha biyar da suka gabata.

“Shugaban ƙasa yana son ya magance wannan matsala gaba ɗaya domin kuɗaɗen da ake kashewa a tsaro su fara amfanar da sauran sassan tattalin arziki kamar wutar lantarki, hanyoyi, ilimi, lafiya da fasahar sadarwa,” in ji shi.

Sai dai jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bukaci fadar shugaban ƙasa ta fito da karin bayani kan dalilan wannan sauyi, tana mai cewa yawan sauye-sauyen cikin gaggawa na iya haifar da ruɗani ko fargaba a cikin tsarin soji.

A shafukan sada zumunta, wasu ‘yan Najeriya sun danganta sauye-sauyen da jita-jitar juyin mulki, yayin da wasu suka bayyana cewa irin wannan sabuntawa abu ne da ake yi lokaci zuwa lokaci a tsarin mulkin soja.

A halin yanzu, Fadar Shugaban Ƙasa ta jaddada cewa wannan mataki na doka ne, tsari ne, kuma ya zama wajibi don ƙarfafa tsaro da zaman lafiya a ƙasar.

No comments