Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Da Zai Gudanar Da Tsara Jana'izar Marigayi Muhammadu Buhari

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu, GCFR ya amince da kafa kwamitin da zai shirya gudanar da jana'izar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhar...


Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu, GCFR ya amince da kafa kwamitin da zai shirya gudanar da jana'izar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, GCFR a gwamnatance.

Kwamitin wanda Sakataren gwamnatin tarayya, George Alume, CON zai jagoranta, an ɗora masa alhakin tsarawa da gudanar da jan'izar Tsohon Shugaban Ƙasan.

Cikin wata ssnarwa da Daraktan hulɗa da jama'a, Segun Imohiosen ya fitar, ta bayyana cewa Mambobin wannan kwamiti sun haɗa da:

i. Ministan Kuɗi

ii. Ministan kasafi da tsara tattalin arziki

iii. Ministan tsaro

iv Ministan yaɗa labarai da wayar kai
 
v.  Ministan ayyuka

vi. Ministan harkokin cikin gida

vii. Ministan Birnin tarayya

viii. Ministan gidaje da raya birane

ix. Ƙaramin Ministan lafiya da jin daɗin jama'a

x. Ministan al'adu

xi. Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro

xii. Babban mashawarci ga shugaban ƙasa a harkokin tsare-tsare da gudanarwa

xiii. Babban mataimaki ga shugaban ƙasa a harkar siyasa da wasu harkoki

xiv. Shugaban 'yan sandan Nijeriya

xv. Shugaban hukumar tsaron farin kaya ta DSS

xvi. Babban Hafsan tsaro na ƙasa

Sannan ofishin babban Sakatare kan al'amuran yau da kullum ne zai kasance matattarar bayanan wannan kwamiti.

Haka kuma, don ƙarin girmamawa ga marigayi Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Shugaba Tinubu ya umurci dukkan ma'aikatun gwamnatin tarayya da su buɗe littafin yin ta'aziyya don ma'aikata su samu damar rubuta ta'aziyyar su na wannan rashi.

Bugu da ƙari, za a buɗe wata rajistar a ma'aikatar kula da ƙasashen wajen, da babban ɗakin taro na Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre, Abuja don baƙi 'yan ƙasashen waje da sauran jama'a su samu damar yin ta su ta'aziyyar.

No comments