Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Kano Ta Samu Ci Gaba A Mulkin Abba Kabir Yusuf Na Shekara Biyu -Habu Muhammad Fagge

  Daga Ibrahim Muhammad, Kano An bayyana cewa Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta yi wani gagarumin yunƙuri...

 

Daga Ibrahim Muhammad, Kano

An bayyana cewa Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta yi wani gagarumin yunƙuri na biyan  haƙƙoƙin ‘yan fansho da suka kammala aiki  shekaru 35 da kuma waɗanda suka rasu a lokacin da suke aiki, wanda ke nuni da irinnl ci gaban da Gwamnan ya samar a shekarun sa biyu yana kulki.

Alhaji Habu Muhammad Fagge, shugaban amintattu na asusun fansho na jihar Kano ne ya bayyana hakan a tattaunawar sa da wakilin ku. Inda ya ce Gwamnatin  Abba Kabir Yusuf ta kawar da matsalolin 'yan fansho ta biya maƙudan  kuɗaɗen 'yan  fansho Naira biliyan 16.

Ya ƙara da cewa yanzu haka ma  akwai Naira  Biliyan Biyar da da suke a ƙasa da za a biya. Ya ce cikin shekaru biyun farko da ga rantsar da shi wanda ya kawo ɗauki ga ɗaruruwan ‘yan fansho da iyalansu.

Alhaji Habibu ya ce, a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, jihar Kano ta samu gagarumin sauyi a harkokin mulki da samar da ayyuka da kuma jagoranci. Jihar ta aiwatar da aikace-aikace da  inganta ababen more rayuwa, farfad)ɗo da ilimi, inganta harkokin kiwon lafiya, da tsare-tsare na ƙarfafa matasa, wanda hakan ya sa  yake samun kyakkyawan  shaidar yabo a kasar baki daya.

"Fitattun nasarori sun haɗa da ayyana dokar ta-baci a fannin ilimi da sanya kaso mai yawa a kasafin kuɗin 2024 da na 2025 ga ilimi da ake ta aiwatar da ayyuka da ke inganta tsarin ilimi. An kuma habaka tsarin kiwon lafiya da inganta  Asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin  farko."

Alhaji Habu Muhammad Fagge ya danganta waɗannan nasarorin da irin yadda Gwamnan ya jajirce wajen kyautata rayuwar al’ummar Kano da kuma dogon hangen nesansa  na samar da ci gaba mai dorewa.

Shugaban  hukumar asusun amintattu na  fansho na jihar Kano ya yi addu’ar Allah ya ci gaba da yi wa Gwamnan da dukkan muƙarraban Gwamnatinsa  jagora wajen ci gaba da  hidimta wa  bunƙasa ci gaban al'ummar Jihar Kano.

No comments