Daga Yusuf Kabir kabiruyusuf533@gmail.com Da safiyar ranar Litinin 25/12/2023 ne wakilan 'yan uwa Musulmi Almajiran Shaikh Ibraheem Zak...
Daga Yusuf Kabir kabiruyusuf533@gmail.com
Da safiyar ranar Litinin 25/12/2023 ne wakilan 'yan uwa Musulmi Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky na garin Samarun Zariya suka ziyarci Cocin TJ.JOSEPH CHATHOLIC da ke Samarun domin taya Kiristoci murnar bikin Kirsimeti na bana.
Wakilin Matattarar Labarai ya labarta mana cewa, a lokacin isar tawagar, ta samu gaharumar tarba daga masu kula da Cocin.
Malam Jamilu Habibu Basawa ne ya yi bayanin dalilin ziyarar cikin harshen Turanci, Sannan ya miĈa abin magana ga Husaini Imam Mansu, wanda shi kuma ya gabatar da tawagar da suka kai ziyarar.
Bayan haka, sai aka miĈa abin magana ga Farfesa Isah Hasan Mshelgaru na Ahmadu Bello ta Zariya domin yin bayanin hadafin ziyarar.
Shehin Malamin Jami'ar ya bayyana dalilin ziyarar cikin harshen Turanci, inda ya bayyana cewa, ''Mun zo ne domin taya ku murnar haihuwar wannan bawa na Allah, wanda shi da Mahaifiyarsa sun kasance ayoyi na Allah a cikin halittarsa.
''HaĈiĈa addinin Musulunci da addinin Kiristanci dukkaninsu suna da alaĈa da juna, kuma mabiyansu su ne galiban mutanen da ke rayuwa a Nijeriya.
"Mu Almajiran Shaikh Ibraheem Ya'qoub Zakzaky (h) ne. A wajen mu dukkanin mutane abin girmamawa ne, domin ko dai 'yan uwan mu a addini ne, ko kuma 'yan uwan mu a halitta."
Farfesan ya ce, sun shekara 25 su na kai irin wannan ziyarar ga Cocina mabambanta a duk sassan Ĉasar nan, musamman a jihohi Arewa, kuma hakan yana da matuĈar amfani. Bugu da Ĉari, hanya ce ta kusantar ma'abuta addinan biyu don samar da zaman lafiya da juna.''
Bayan kammala jawabin Farfesa Isah, sai aka gabatar da Fitaccen mawakin Harkar Musulunci Malam Ammar Ĉantinka Zariya, inda ya rero daÉaÉan baituka ga Annabi Isah Almasihu (as), a yayin da makaÉan Cocin suka kiÉa gangunan su domin Ĉara wa waĈar armashi.
Bayan kammala waĈen, an gabatar da Dr. Salisu Ahmad, Malami a Jami'ar Umaru Musa 'Yar Aduwa domin ya Ĉaddamar da kyautukan da maziyartan suka kai wa masu hidimar bikin. A yayin da Faston Cocin da Éansa suka karÉa cikin farin ciki da annashuwa.
Daga nan ne kuma sai aka miĈa abin magana ga Malam Jamilu Habibu Basawa, a yayin da ya gayyato Faston Cocin haÉe da Farfesa Isah Hasan Mshelgaru, Dr. Salisu Ahmad, Alhaji Mansur Ali, Ammar Ĉantinka suka yanka Alkaki cikin farin ciki.
Bayan kammala hakan, Éaya daga cikin Shugabannin Cocin ya yi bayanin godiya, inda ya miĈa abin magana ga Fasto ya yi bayani mai ratsa jiki da nuna jin daÉi ga ziyarar da 'yan uwa Musulmi suka gabatar, inda ya bayyana jin daÉin karramawar da aka yi musu, ciki kuwa har da yanka Alkaki.
Wani abin da wakilinmu ya lura da shi da ya Ĉara wa ziyarar armashi, shi ne gayyatar wakilan kafafen yaÉa labarai daban daban-daban da aka yi domin su Éauki rahotannin ziyarar, tare da watsawa cikin al'umma.
Malam Bello Hamza Editan Jaridar Leadership Hausa, Mustapha Yawuri daga kafar NAN (tare da tawagarsa), Sagir Hunkuyi daga NTA, Yusuf Kabir daga Jaridar Almizan na cikin 'yan Jaridar da suka rufa wa tawagar baya.
WaÉanda aka kai wa ziyarar sun nuna matuĈar farin cikin su.
No comments