Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

2027: Mainasara Salga Ya Lashe Tikitin ADC Na Majalisar Tarayya Daga Kano

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Hon. Abdurrahman Mansur Mainasara Salga ne ya lashe zaben fitar da gwani na jam’iyyar African Democratic Congres...

Daga Ibrahim Muhammad, Kano

Hon. Abdurrahman Mansur Mainasara Salga ne ya lashe zaben fitar da gwani na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) domin tsayawa takar majalisar tarayya a Ĉ˜aramar Hukumar Dala ta jihar Kano, bayan ya samu Ĉ™uri’u 8,973.

Zaben wanda aka gudanar a ranar 21 ga Mayu, 2026, ya gudana bisa tsarin Ĉ™ato bayan Ĉ™ato Ĉ™arĈ™ashin jagorancin dokar Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ĉ˜asa (INEC). 'Yan takara uku ne suka fafata: Hon. Abdurrahman Mansur Mainasara Salga, Hon. Nasir Isa, da Hon. Bashir Muhammad.

A Ĉ™arĈ™ashin kulawar wakilan uwar jam’iyyar ta Ĉ™asa, Ĉ™ungiyoyin sa-ido da jami’an tsaro, maza da mata mambobin ADC a Dala sun fito domin kaɗa Ĉ™uri’ar su cikin kwanciyar hankali.

Bayan kammala zaben, kwamitin gudanarwa ya bayyana sakamakon haka: Hon. Nasir Isa ya samu kuri’u 821, Hon. Bashir Muhammad ya samu kuri’u 1,584, yayin da Hon. Amb. Abdurrahman Mansur Mainasara Salga ya zama na ɗaya da Ĉ™uri’u 8,973 daga cikin jimillar Ĉ™uri’u 11,377 da aka kaɗa.

Dangane da haka, an tabbatar da Mainasara Salga a matsayin dan takar ADC na majalisar tarayya mai wakiltar Dala a zaben 2027.

Da yake jawabii kan nasarar da ya samu Hon. Mainasara Salga ya nuna godiyar sa ga mambobin jam’iyyar a Dala bisa goyon bayan da suka ba shi. Ya kuma buĈ™aci sauran yan takara da ya fafata da su da su hada kai domin Ĉ™arfafa jam’iyyar ADC domin cimma nasara a zaben 2027.
 

No comments