Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Ɗangote Ya Nuna Damuwa Kan Kuɗin Ruwa Da Babban Banki Ya Ƙara Wa Masana'antu

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Shugaban rukunin kamfanonin Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya nuna damuwarsa game da kuɗin ruwa na kusan kashi 3...

Daga Ibrahim Muhammad, Kano

Shugaban rukunin kamfanonin Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya nuna damuwarsa game da kuɗin ruwa na kusan kashi 30 cikin 100 da babban bankin Nijeriya ya ƙara ga masana'antu, yana mai kira ga gwamnati da ta tallafa  wajen haɓaka  kamfanoni.

Ya  bayyana hakan ne  a taron ƙungiyar masu masana'antu na ƙasa da aka yi a Abuja, inda ya yi gargaɗin cewa, “Babu wanda zai iya samar da ayyukan yi da kuɗin ruwa na kashi 30 babu wani ci gaba  da za a samu.

Daga nan Attajirin ya jaddada buƙatar samar da kuɗaɗe da kuma Samar da  kariya ga masana’antun cikin gida su ƙara haɓaka domin rage dogaro da shigo da kaya, wanda hakan yana ƙara haifar da fatara da rashin ayyuka.

Alhaji Aliko Ɗangote ya jaddada muhimmancin tallafa wa masana’antu na  gida don yaƙar rashin tsaro da samar da wadatar arziki.

 

No comments